Bakonmu A Yau

Informações:

Sinopsis

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.

Episodios

  • Arewacin Najeriya aka fi kashe mutane a zangon farko na wannan shekarar - Rahoto

    23/04/2024 Duración: 03min

    Wani bincike da kamfanin Beacon Securities ya yi a Najeriya, ya ce a watanni 3 na farkon wannan shekarar an kashe mutane sama da 2,500, yayin da aka yi garkuwa da wasu sama da dubu 2. Rahotan ya ce kashi 80 na wannan aika aika ana samun sa ne a yankin Arewacin Najeriya. Dangane da haka Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya.  Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawar su ta gudana......

  • Farfesa Mansur Isa Yelwa kan tsarin almajiranci a Najeriya

    22/04/2024 Duración: 03min

    A karshen makon da ya gabata ne zabtarewar kasa ta hallaka wasu almajirai guda 8 a Jihar Kebbi, matsalar da ta dada  tado da batun kula da almajiran da ke karatun Alkur'ani. Wasu na danganta matsalar da sakacin iyaye wajen rashin kula da 'ya'yan su ko kuma ciyar da su a makarantun allon. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Frafesa Mansur Isa Yelwa, daya daga cikin manyan malaman addinin Musulunci kuma masanin shari'a a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawarsu.......

  • Arewa maso Yammacin Najeriya ne mafi hatsari saboda matsalar tsaro - Bincike

    18/04/2024 Duración: 03min

    Kungiyar 'Global Rights' ta bayyana yankin arewa maso yammacin Najeriya a matsayin mafi hadari, saboda yadda 'yan bindiga ke kisa da take hakkin Bil Adama ba tare da kaukautawa ba. Kungiyar tace a cikin shekaru 10 da suka gabata, yankin ya gamu da mummanar ukuba, fiye da sauran sassan Najeriya.Bashir Ibrahim Idris ya tintibi Dr Murtala Ahmad Rufai na Jami'ar Usman Danfodio, mawallafin 'I am a Bandit' kuma mai bincike a kan matsalar tsaron yankin.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

  • Kuskure ne a yi tunanin ɗagawar darajar naira ba zai ɗore ba - Dakta Kurfi

    17/04/2024 Duración: 03min

    Darajar Naira na cigaba da ɗagawa a Najeriya tare da saukar farashin wasu kayayyakin abinci a wasu kasuwannin ƙasar, abinda ya sa wasu tunanin cewar tasirin saukar Dalar ne ya sanya wasu kayayyakin suka fara sauka. Wane hasashe masana tattalin arziƙi ke yi game da ci gaba da ɗagawar darajar Nairar, tare da zubewar Dala? Tambayar kenan da Abdulkadir Haladu Kiyawa, ya yi wa Dakta Ƙasim Garba Kurfi masanin tattalin arziki a Najeriya yayin tattaunawarsu.

página 2 de 2